Isa ga babban shafi
Somalia

Mutane sun mutu a kazamin harin Somalia

Akalla mutane 6 sun rasa rayukansu yayin da wasu 16 suka jikkata bayan wata mota makare da bama-bamai ta tarwatse a harabar ofishin gwamnati da ke birnin Mogadishu na Somalia.

Kungiyar al Shebaab ta dauki alhakin kaddamar da farmakin da ya lakume rayuka 6 a Somalia
Kungiyar al Shebaab ta dauki alhakin kaddamar da farmakin da ya lakume rayuka 6 a Somalia REUTERS/Feisal Omar
Talla

Wani babban jami’in ‘yan sanda, Ibrahim Mohamed ya bayyana cewa, motar ta yi karo da shingen bincike na jami’an tsaro a dab da shalkwatan gwamnatin yankin Hodan kafin daga bisani ta tarwatse.

Tarwatsewar motar ta rusa gine-gine da dama da suka hada da masallaci, yayin da hayaki mai kauri ya turnuke sararin samaniya.

Shaidu sun ce, an yi ta zakulo gawarwaki daga karkashin buragunzan gine-ginen da suka rushe a sanadiyar harin wanda kungiyar al-Shebaab ta dauki alhakin kaddamarwa.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.