Isa ga babban shafi
Somalia

Mayakan Al Shabaab sun sake kai hari a birnin Mogadishu

Rundunar ‘yan sandan Somalia ta ce tagwayen hare-haren bam da aka kai kan ma’aikatar tsaron cikin gidan kasar da ke birnin Mogadishu, sun yi sanadin hallakar fararen hula 5 da jami’in dan sanda daya.

Jami'an tsaron Somalia a birnin Mogadishu, yayin da suke kokarin yi wa harabar da dan kunar bakin wake ya tarwatsa wata mota kawanya.
Jami'an tsaron Somalia a birnin Mogadishu, yayin da suke kokarin yi wa harabar da dan kunar bakin wake ya tarwatsa wata mota kawanya. REUTERS/Feisal Omar
Talla

Harin dai shi ne na baya bayan nan da kungiyar al Shebaab ta yi dauki alhakin kai wa a kasar ta Somalia.

Kwamandan ‘yan sandan birnin Mogadishu, Ibrahim Muhd, baya ga wadanda suka hallaka, akalla mutane 21 sun jikkata a harin, sai dai sun yi nasarar hallaka baki dayan mayaka hudu na kungiyar ta Al Shebaab da suka kai harin ciki harda dan kunar bakin wake daya.

Duk da rasa yankunan da ta kame a baya, bayan shafe sama da shekaru 10 tana kokarin kawar da gwamnatin Somalia, har yanzu kungiyar al Shebaab na samun karfin kai hare-haren kunar bakin wake da kuma samamen ‘yan bindiga kan ma’aikatun gwamnatin kasar da kuma wuraren cinkoson fararen hula.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.