An rantsar da sabon Shugaban Zimbabwe
A yau juma’a aka rantsar da Emmerson Mnangagwa a matsayin shugaban kasar Zimbabwe, bayan kawo karshen mulkin Robert Mugabe na tsawon shekaru 37.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
An yi bikin rantsar da Mnangagwa a filin wasa da ke babban birnin kasar Harare, bayan dawowarsa gida a ranar Laraba, daga gudun hijirar da ya yi zuwa Afrika ta Kudu, sakamakon korar shi daga mukamin mataimakin shugaban kasa da Mugabe ya yi a farkon watan da muke ciki.
Korar da Mugabe ya yi Mnangagwa, ta taka rawa wajen sanya jam’iyya, mai mulkin kasar ZANU-PF da kuma rundunar sojojin kasar yin ruwa da tsaki wajen kawo karshen rudanin siyasar kasar, bayan da Mugabe ya rubuta takardar Murabus.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu