Isa ga babban shafi
AU

Tarayyar Afrika ta goyi bayan yarjejeniyar Paris ta canjin yanayi

Kungiyar Tarayyar Afirka AU ta bayyana cikakken goyan bayanta ga yarjejeniyar magance matsalar sauyin yanayin da aka kulla a Paris, tare da yin allawadai da matsayin shugaba Donald Trump na yin watsi da yarjejeniyar.

Shugaban Guinea Alpha Conde kuma shugaban Tarayyar Afrika
Shugaban Guinea Alpha Conde kuma shugaban Tarayyar Afrika
Talla

Kungiyar AU ta ce gurbata yanayin da masana’ntun manyan kasashe ke yi, ya fi yi wa nahiyar illa a duniya.

Shugaban Guinea kuma shugaban kungiyar Alpha Conde ya bukaci a tattauna batun canjin yanayin a taron kasashe 20 masu karfin tattalin arziki na G20 da za a gudanar a Jamus a watan gobe.

Shugaba Conde ya ce akwai bukatar a wayar wa Trump kai kan illolin dumamar yanayi a duniya.

A ranar Alhamis ne shugaban Amurka Donald Trump ya sanar da yin watsi da yarjejeniyar ta Paris da aka amince a 2015.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.