Sudan ta kudu
Sabon rikici ya barke a Sudan ta Kudu.
Rahotanni daga Sudan ta kudu sun ce an samu barkewar tashin hankali a Malakal, birni na biyu mafi girma a kasar kuma cibiyar hakar man fetur.
Wallafawa ranar:
Talla
Kakakin sojin Sudan ta kudu Kanar Santo Domic Chol ya ce ‘Yan tawayen sun dadde suna neman tayar da hankali bayan zaman lafiyan da aka samu a Yankin.
Sai dai kakakin ‘yan tawayen Gatjiath Deng ya zargi sojojin ne da kaddamar da haria sansanin su.
Deng ya ce dakarun su sun yi nasarar kassara sojojin gwamnati a karawar da akayi.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu