Isa ga babban shafi
Sudan ta kudu

Sabon rikici ya barke a Sudan ta Kudu.

Rahotanni daga Sudan ta kudu sun ce an samu barkewar tashin hankali a Malakal, birni na biyu mafi girma a kasar kuma cibiyar hakar man fetur.

Ana zargin 'yan tawaye da tayar da rikici a Sudan ta Kudu.
Ana zargin 'yan tawaye da tayar da rikici a Sudan ta Kudu. REUTERS/James Akena
Talla

Kakakin sojin Sudan ta kudu Kanar Santo Domic Chol ya ce ‘Yan tawayen sun dadde suna neman tayar da hankali bayan zaman lafiyan da aka samu a Yankin.

Sai dai kakakin ‘yan tawayen Gatjiath Deng ya zargi sojojin ne da kaddamar da haria sansanin su.

Deng ya ce dakarun su sun yi nasarar kassara sojojin gwamnati a karawar da akayi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.