An cire Isaac Zida daga cikin sojojin Burkina Faso
A Burkina Faso gwamnatin kasar a yau juma”a ta sanar da cire sunan Isaac Zida tsohon firaministan kasar daga cikin sunayen sojojin kasar bayan da ta same shi da laifin kin zuwa wajen aiki tareda gudu zuwa kasar waje .
Wallafawa ranar:
Shugaban kasar Burkina Faso da kan sa ne ya aike da kira zuwa Isaac Zida wanda ke samu mafaka a kasar Canada ,wanda daga bisali ya bijerewa kiran shugaban kasar.
Wasu yan kasar dama masu lura da al’amuran siyasar Burkina Faso sun bayyana cewa tsohon Firaministan Isaac Zida na da hannu a batutuwa da suka shafi rub da ciki a kasar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu