Isa ga babban shafi
Faransa-Sahel

Faransa za ta kara kaimin yakar ‘Yan ta’adda a Sahel

Firaministan Faransa Bernard Cazeneuve da ke ziyara a kasashen Sahel ya ce Faransa za ta kara yawan kasafin tsaro ga sojojinta da ke yaki da ta’addanci a yankin.

Firaministan Faransa Bernard Cazeneuve da Ministan tsaro Jean-Yves Le Drian suna ganawa da rundunar "Barkhane a N'Djamena kasar Chadi
Firaministan Faransa Bernard Cazeneuve da Ministan tsaro Jean-Yves Le Drian suna ganawa da rundunar "Barkhane a N'Djamena kasar Chadi REUTERS
Talla

Bernard Cazeneuve ya fadi haka ne a N’Djamena, a ziyarar farko da ya kai a yankin  Sahel a matsayin Firaminsitan Faransa.

Firaministan ya ce za su ci gaba daukar matakan da za su dore ga tabbatar da tsaron Faransa.

Sannan ya ce Faransa za ta kasance a cikin shirin yaki a kodayaushe kuma a ko wane yanki har sai an kakkabe ‘Yan ta’adda.

Cazeneuve dai na amfani da ziyara ne domin sake jaddada goyan bayan Faransa a yaki da ta’adanci tare da sake duba sabbin hanyoyin karfafa hulda da kasashen Sahel ta fuskar tsaro.

Faransa na da dakaru kimanin 4,000 a kasashen Mouritania da Nijar da Mali da Burkina Faso da kuma Chadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.