Isa ga babban shafi
Libya

Gwamnatin Libya ta sanar da mallakar Sirte a hukumance

Gwamnatin hadin kan Libya da ke samun goyon bayan Majalisar Dinkin Duniya, ta sanar da kawo karshen ayyukan sojinta a birnin Sirte, bayan samun nasarar kakkabe mayakan IS daga cikinsa.

Birnin Sirte na Libya da yaki ya rusa
Birnin Sirte na Libya da yaki ya rusa
Talla

Sai dai kuma Firaministan kasar Fayez al-Sarraj yayi gargadin cewa hakan ba yana nufin sun kawo karshen yaki da mayakan na IS bane.

Sojin Libya sun shafe watanni takwas kafin samun wannan nasara, inda a ranar 5 ga watan Disamba sojin kasar, suka sanar da karbe ikon birnin na Sirte daga hannun kungiyar IS, wanda ya zamo tungar kuniyar mafi karfi kuma ta karshe a kasar.

Kwace birnin Sirte, mahaifar tsohon shugaban kasar Mu'ammar Gaddafi daga mayakan IS, babban koma baya ne garesu, duba da murkushe su da ake cigaba da yi a kasashen, Syria da Iraqi.

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.