Sarkin Morocco ya gargadi Musulmin kasar
Sarkin Moroko Muhammaed na 6, ya yi kira ga Musulmin kasar dake zama a kasashen waje dasu rugumin tsarin musulunci da kauracewa duk wani abu da zai batawa addinisu sunan.
Wallafawa ranar:
Sarki Muhammaed dake allawadai da aikata kisa kan wadanda basu jiba basu gani ba, ya kuma bayyana takaicinsa kan kisan limamin Cocin Faransa da yace ba abu bane da ba za a yafewa Maharin.
Wanna shi ne karo na farko da sarki Muhammad ya yi kira ga al'umar kasar a duk inda suke a fadin duniya, a wani mataki na wayar da kan su sakamakon hare-hare da masu kishin islama ke kaiwa a kassahen turai.
Hare-haren dai sun rutsa da wasu daga cikin 'yan Morocco mazauna kasashen turai.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu