Isa ga babban shafi
Faransa-Maroko

Shugaba Francois Hollande na ziyarar aiki a Maroko

A yau asabar shugaban Fransa Francois Hollande zai fara ziyarar aiki a birnin Tanger na kasar Maroko, domin karba gayyatar sarkin kasar Mohammed na shida.

Mohammed na shida da François Hollande a fadar Elysée ranar 9 ga watan fabarairun 2015.
Mohammed na shida da François Hollande a fadar Elysée ranar 9 ga watan fabarairun 2015. REUTERS/Philippe Wojazer
Talla

Majiyoyin diflomasiyya sun bayyana cewa batun tattalin arziki da kuma sauyin yanayi, na daga cikin muhimman batutuwan da shugabannin kasashen biyu za su mayar da hankali a lokacin wannan ziyara.

Har ila yau ziyarar za ta kasance wata dama ga kasashen biyu domin warware sabanin da suka sama a shekarar bara, bayan da wani alkalin Faransa ya bukaci shugaban hukumar leken asirin Maroko ya gurfana a gabansa bisa zargin cin zarafin bil’adama.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.