Isa ga babban shafi
Sudan ta Kudu

Majalisar Dinkin Duniya zata bincike Sudan ta Kudu

Majalisar Dinkin Duniya ta kadadmar da bincike kan harin da Yan Tawayen Sudan ta kudu suka kai wani otel dake Juba, inda suka kashe wani dan Jarida suka kuma yiwa mata fyade lokacin da aka fafata tsakanin su da sojojin gwamnati.

Wasu daga cikin makaman da sojin Sudan ta Kudu suka kwace daga 'yan tawaye
Wasu daga cikin makaman da sojin Sudan ta Kudu suka kwace daga 'yan tawaye AFP/Ashraf Shazly
Talla

Ana zargin sojojin Majalisar ne da kasa kai dauki dan kare fararen hular dake cikin wani otel da ake kira Hotel Terrain dake Juba duk da yake an shaida musu lokacin da fadan ya kazance.

Ban ki Moon ya bayyana takaicin sa dangane da zargin da aka yiwa sojojin samar da zaman lafiyar.

Majalisar dinkin Duniya ta sha zargin sojin gwamnati da bangaren 'yan tawayen kasar Sudan ta Kudu da aikata laifukan yaki, lamarin da yake kara rura wutar rikici a kasar.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.