China
An sace ‘Yan China biyu a Abuja
‘Yan sanda a Najeriya sun ce Wasu ‘Yan bindiga sun sace wasu ‘Yan China guda biyu a Abuja. Rundunar ‘Yan sandan Jihar Nasarawa ta ce an sace ‘Yan China ne a jiya Asabar a wani harin kwantar bauna da ‘Yan bindigar suka kai masu a daidai kauyen Agada akan hanyarsu ta zuwa Abuja.
Wallafawa ranar:
Talla
Bayanai sun ce ‘Yan Chinan ma’aikata ne na wani kamfanin ayyuka a yankin da ke tsakanin Abuja da Nasarawa.
Babu dai cikakken bayani akan ‘Yan bindigar.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu