Isa ga babban shafi
Nijar

Shekaru 56 da samun ‘yancin Nijar

Yau 3 ga watan Agusta al’ummar Jamhuriyar Nijar ke bukin cika shekaru 56 da samun ‘yancin kai daga Turawan Faransa da suka yi wa kasar mulkin mallaka.

Shugaban Nijar Issoufou Mahamadou
Shugaban Nijar Issoufou Mahamadou BOUREIMA HAMA / AFP
Talla

Nijar ta samu ‘Yancin kai ne a 1960.

Shugaban kasa Mahammadu Issoufou, ya yi wa ‘yan kasar jawabi, inda ya tabo kokarin da ya ke yi ta fannin tsaro da kiwon lafiya da ilmi.

A cikin jawabin, shugaban ya jajantawa iyalan Sojojin Nijar da suka mutu a yaki da Mayakan Boko Haram.

Shugaba Issoufou ya jaddada burin shi na kawar da yunwa ta hanyar tsarin dan Nijar ya ci da dan Nijar.

Ana amfani da ranar domin shuka itace don magance kwararowar Hamada kuma Sojojin da suka hambarar da gwamnatin Diori Hamani a 1975 suka bukaci shuka itacen.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.