Isa ga babban shafi
Faransa-Najeriya-boko haram

Taron shugabanin kasashe dake yakar Boko Haram a Abuja

Shugaban Faransa Francois Hollande ya samu isowa babban birnin tarrayar Najeriya Abuja,domin halartar taron kasashen dake yaki da kungiyar Boko Haram.

Taron shuganin kasashen a Abuja
Taron shuganin kasashen a Abuja REUTERS/Afolabi Sotunde
Talla

Wanan gangami na Abuja zai hada Shugabanin kasashe da za su yi bitar kokarin dama ci gaba da aka samu dangane da batun kawo karshen wannan kungiya ta Boko Haram .

Hollande Shugaban na Faransa da ya samu yada zango a jiya a kasar Afrika ta Tsakiya, a zantawarsa da hukumomin kasar ya sanar da matsayi faransa na cewa zata janye dakarun ta dake karkashin rundunar Sangaris, shugaban ya kuma tabbatar da cewa kasar sa zata ci gaba da kawo gudunmuwa dama horo kan batutuwan tsaro a kasashen Afrika.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.