Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojin Najeriya na horar da 'yan Boko Haram 800

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya ta ce, rundunar sojin kasar na horar da mayakan Boko Haram akalla 800 bayan sun tuba tare da ajiye makamansa domin karbar zaman lafiya a yankin arewa maso gabashin kasar.

Shugaban sojojin kasa na Najeriya, Laftanar Tukur  Yusuf Buratai.
Shugaban sojojin kasa na Najeriya, Laftanar Tukur Yusuf Buratai. AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Rundunar dai na aikin sauya tunanin tsoffin mayakan ne domin su yi rayuwa mai inganci a tsakanin al’umma.

Hukumar ta NEMA ta ce, ana aikin wayar mu su da kai ne a karkashin wani shiri mai taken "Safe Corridor Initiative" kuma karkashin kulawar ofishin babban hafsan sojin kasar.

Wannan na zuwa ne a yayin da majalisaer dattawan kasar ke shirin amince wa da kudirin samar da hukumar farfado da yankin arewa maso gabashin Najeriya a ranar 25 ga wannan wata na mayu.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.