Isa ga babban shafi
Boko Haram

‘Yan gudun hijira na fama da yunwa a tafkin Chadi

Yunwa da tsoron harin kungiyar Boko Haram na ci gaba da zama barazana ga dubban ‘yan gudun hijirar da rikicin Boko haram ya ritsa da su a Yankin tafkin Chadi.

Yankin Ngouboua, a Tafkin Chadi da 'Yan Boko Haram suka taba kai hari
Yankin Ngouboua, a Tafkin Chadi da 'Yan Boko Haram suka taba kai hari AFP PHOTO / STEPHANE YAS
Talla

Florent Mehaule, jami’in aikin jinkai na Majalisar Dinkin Duniya a garin Baga Sola ya ce akalla ‘yan gudun hijira 110,000 ke rayuwa a sansanonin da ‘yan gudun hijira suka samarwa kansu a gabar ruwan tafkin Chadi da ya kewaye kasashen Najeriya da Nijar da Kamaru da kuma Chadi.

Jami’in yace duk da jami’an tsaron da ke kula da su ana samun hare hare nan da can abin da ke razana mutanen da ke sansanin.

Sannan ‘Yan gudun hijira na fama da yunwa a yayin da suke zaman zullumi da fargabar yiyuwar hare haren yan Boko Haram.

An dai taba kai hare haren kunar bakin wake a garin Baga Sola a watan Oktoba inda aka kashe mutane 41.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.