Isa ga babban shafi
Tafkin Chadi

An kashe mutane 27 a hare haren kunar bakin wake a tafkin Chadi

Akalla mutane 27 Sun mutu yayin da wasu 80 suka jikkata a wasu jerin hare haren kunar bakin wake guda uku da aka kai a yankin tafkin Chadi a ranar Assabar. Ana daura alhakin hare-haren akan mayakan Boko Haram.

'Yan Boko Haram sun addabi yankin tafkin Chadi da hare hare
'Yan Boko Haram sun addabi yankin tafkin Chadi da hare hare AFP PHOTO / PHILIPPE DESMAZES
Talla

Wata majiyar Sojin Chadi ta shaidawa kamfanin dillacin labaran Faransa cewa ‘yan kunar bakin waken sun kai hare-haren ne a wurare daban daban cikin wata kasuwar Loulou Fou da ake ci mako mako.

Mayakan Boko Haram dai sun dade suna addabar Yankin tafkin Chadi wanda ke cikin dokar ta-baci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.