Najeriya ta goyi bayan kafa kasar Falasdinu
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya bayyana goyan bayan sa na ganin an kafa kasar Falasdinu dan kawo karshen matsalolin da Falasdinawa ke fuskanta a Gabas ta Tsakiya.
Wallafawa ranar:
Yayin da ya ke ganawa da Sarkin Qatar Sheikh Tamim bin Hammad al Thani, shugaba Buhari ya ce Najeriya na goyan bayan daukacin kudirorin da Majalisar Dinkin Duniya ta amince da su wajen samun kasashe biyu tsakanin Israila da Falasdinu.
Buhari ya shaidawa Sarkin cewar Najeriya za ta hada kai da Qatar har sai ta ga Falasdinu ta samu biyan bukata.
Idan dai ba’a manta ba a shekarar da ta gabata, Najeriya taki kada kuri’ar goyan bayan Falasdinu a kwamitin Sulhu a karkashin shugabancin Goodluck Jonathan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu