Isa ga babban shafi
Isra'ila-Falasdinawa

Furgaban barkewar sabuwar rikici tsakanin Falasdinawa da Isra'ila

Tun ranar Assabar da ta gabata wasu garuruwa da ke gabar yammacin kogin Jodan, da kuma wasu unguwannin dake gabashin birnin Kudus ke arangama da matasan Falasdinawa da ke tunawa da zagayowar ranar ‘’Intifada’’ da aka Assasa gwagwarmayar Falasdinawa a shekarar 1987 da kuma  shekarar 2000

Matasan Falasdinawa na tunkarar sojojin Israela da duwatsu
Matasan Falasdinawa na tunkarar sojojin Israela da duwatsu REUTERS/Mohamad Torokman
Talla

Intifadar dai ta soma ne, da jifar duwatsu da  kwalaben   ''aci-balbal'' daga matasan falasdinawa, a yayin da su kuma  sojojin Isra'ila suka mayar da martani da harbin bindiga, al’amarin da ya yi sanadiyar mutuwar Falasdinawa 48 wasu 150 kuma suka jikkata.

A jiya litinin dai wata sabuwar tarzomar ta kara barke a gabar yammacin kogin Jodan.

Intifada da ke nufin Bore da larabci, ko kuma yaki ta hanyar jifa da duwatsu da Falasdinawa ke yi, ya fara ne tun a shekarar 1987 sanadiyar wata babbar motar dakon kaya ta kasar Isra'ila da ta markade wata motar falasdinawa  tare da kashe daukacin Falasdinawan 4 da ke cikin motar.

Wannan dai shine masomin farko na barkewar gwagwarmayar ta Intifada, neman yancin kan falasdinawa a yankunan da Isra'ila ta mamaye.

Hotunan da suka zagaya duniya na  rashin imani da Isra'ila ta  nuna a kan Falasdinawan dai,  ya yi matukar tunzura wasu kasashe  da kuma wasu  kungiyoyin da ke hankoron kare hakkin dan adam na duniya a wancan lokaci.

 

 

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.