Falasdinawa na zargin Hamas da shiga tattaunar sirri da Isra’ila
Mahukuntan Falasdinawa a Ramallah sun zargi kungiyar Hamas da ke iko a Gaza da shiga tattaunawar sirri da gwamnatin Isra’ila kan shirin raba Yankunan Falasdinawa.
Wallafawa ranar:
Ministan harkokin wajen Falasdinawa Riad al Malik ya ce akwai tattaunawar siri da bangarorin biyu ke yi, kuma sun kusa kulla yarjejeniyar tsagaita wuta na shekaru 8 zuwa 10, matakin da zai sa Israila ta cire shingen da ta sa a Gaza tare da da barin jiragen ruwa wucewa zuwa Cyprus.
Wata majiyar Hamas ta amince da cewar suna musayar ra’ayi da Isra’ila ta bayan-fage amma batun ayyukan jinkai kawai suka tattauna.
Sai dai kuma gwamnatin Isra’ila ta ce babu wata tattaunawa da ta ke yi da Hamas, kungiyar da ta danganta a matsayin ta ‘Yan ta’adda.
Kungiyoyin Hamas da Fatah ne dai ke shugabanci a yankunan Falasdinawa guda biyu, Gaza da gabar yamma da kogin Jordan.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu