Isa ga babban shafi
Afrika taTsakiya

‘Yan takara za su kammala yakin neman zabe a CAR

A yau Litinin ake kammala yakin neman zaben shugaban kasa da na Yan Majalisu a kasar Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya mai fama da tashin hankali.

a ranar 13 ga Disemba al'ummar Afrika ta tsakiya sun amince da sabon kundin tsarin mulki da ake ganin zai kawo karshen rikici mai nasaba da addini a kasar
a ranar 13 ga Disemba al'ummar Afrika ta tsakiya sun amince da sabon kundin tsarin mulki da ake ganin zai kawo karshen rikici mai nasaba da addini a kasar MARCO LONGARI / AFP
Talla

A ranar Laraba ne 30 ga watan Disemba al’ummar kasar za su kada kuri’a domin zaben sabon shugaba.

‘Yan takaran shugaban kasa 30 ke fafatawa don neman shugabancin kasar da ta fada cikin tashin hankalin kabilanci da addini shekaru uku da suka gabata.

Kungiyar kasashen Afrika da Majalisar Dinkin Duniya sun yi kira ga al’ummar kasar su kai zuciya nesa wajen ganin an yi zaben cikin kwanciyar hankali.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.