Isa ga babban shafi
Afrika taTsakiya

‘Yan Afrika ta tsakiya sun amince da sabon kundin tsarin mulki

Sakamakon Zaben raba gardama a Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya ya nuna cewar kashi 93 na al’ummar kasar sun amince da sabon kundin tsarin mulkin da aka rubuta.

A ranar 14 ga watan Disemba ne aka gudanar da zaben raba gardama
A ranar 14 ga watan Disemba ne aka gudanar da zaben raba gardama MARCO LONGARI / AFP
Talla

Sabon kundin ya kunshi wa’adin shugabancin kasar sau biyu da yaki da cin hanci da rashawa da murkushe masu dauke da makamai.

Sakamakon zaben zai dada karfafa shirin zaben shugaban kasar da na ‘Yan Majalisu da za a gudanar a cewar shugaban hukumar zabe Marie Madeleine N’Kouet Hoornet.

Yanzu haka ‘Yan takara 30 ne suka kaddamar da yakin neman zaben shugaban kasa da za a gudanar a ranar Lahadi bayan al’ummar kasar sun amince da sabon kundin tsarin mulki.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.