Isa ga babban shafi
Afrika ta tsakiya

Rikici ya dagula zaben raba gardama a Bangui

Akalla mutane biyu suka mutu a rikicin da ya barke a Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya a yayin da ake gudanar da zaben raba gardama kan sabunta kundin tsarin mulki.

An yi zaben raba gardama cikin rikici a Bangui
An yi zaben raba gardama cikin rikici a Bangui
Talla

Rikicin ya barke ne a yankunan Musulmi a Bangui tsakanin masu sabanin ra’ayi akan sabon kundin tsarin mulkin.

Sannan an yi harbe-harbe da manyan bindigogi tare da harba makamin roka a wata Makaranta da mutane ke jiran su kada kuri’a.

Zaben dai ya kasance zakaran gwajin dafi ga zaben shugaban kasa da na ‘Yan Majalisu da za a gudanar a ranar 27 ga watan Disemba.

Sabon kundin tsarin mulkin da ‘Yan kasar za su amince ya kunshi takaita wa’adin shugabancin kasar zuwa wa’adi biyu, tare da kaddamar da yaki da cin hanci da rage karfin kungiyoyin kasar masu dauke da makamai.

An shafe shekaru biyu Afrika ta tsakiya na cikin rikici mai nasaba da addini tsakanin Mayakan Seleka musulmi da kuma anti-Balaka kiristoci.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.