Isa ga babban shafi
Jamhuriyar Afrika ta Tsakkiya

Tarzoma ta barke a Afrika ta tsakiya kan takarar shugabanci Bozize

Sabuwar tarzoma ta kunno kai a birnin Bangui na Jamhuriyar Afrika ta tsakiya, inda masu zanga-zanga suka kafa shingaye a tsakiyar hanya.Rikicin ya biyo bayan umarni da kotun fasalta kundin tsarin mulkin kasar ta yanke na haramtawa tsohon shugaban kasar Francois Bozize tsaya wa takarar a zaben shugabancin kasar da za a gudanar a ranar 27 ga watan Disamba shekarar nan. 

Kotu ta haramtawa François Bozizé tsayawa takarar shugabanci kasar Afrika ta Tsakiya
Kotu ta haramtawa François Bozizé tsayawa takarar shugabanci kasar Afrika ta Tsakiya Africanarguments.org
Talla

Rahotanni sun ce anyi ta jin karar harbe-harben bindiga a yankuna takwas na birnin yayin da kasar Faransa ta bukaci al-ummarta da su kaurace wa yankunan.

A na dai kyautata zaton cewa zaben zai dawo da kwanciyar hakankali a kasar wadda ta shafe shekaru biyu tana fuskantar rikici tsakanin Musulmai da Krista.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.