Isa ga babban shafi
Afrika ta tsakiya

Ana zaben raba gardama a Afrika ta tsakiya

Al’ummar kasar Jamhuriyyar Afrika ta tsakiya mai fama da rikici na jefa kuri’ar zaben raba gardama a yau Lahadi kan sabon kundin tsarin mulki wanda ake ganin tamkar zakaran gwajin dafi ga samar da zaman lafiya a kasar.

Mutane da dama aka kashe a Afrika ta tsakiya a rikici mai nasaba da addini tsakanin Mayakan Seleka musulmi da anti balaka Kiristoci
Mutane da dama aka kashe a Afrika ta tsakiya a rikici mai nasaba da addini tsakanin Mayakan Seleka musulmi da anti balaka Kiristoci RFI/Pierre Pinto
Talla

Zaben na zuwa ne duka makwanni biyu da Fafaroma Francis ya kai ziyara a Bangui inda ya yi kira ga al’ummar Musulmi da Kirista a kasar su zauna lafiya a matsayin ‘yan uwan juna.

Rikici dai ya hana aiwatar da cikkakken tsarin gudanar da zaben.

Kuma yanzu haka kalilan ne ke da masaniya ga abinda sabon kundin tsarin mulkin ya kunsa domin kwafi 15,000 aka buga kamin soma zaben.

Afrika ta tsakiya ta fada cikin rikici ne a 2013 bayan ‘Yan tawayen Seleka yawancinsu Musulmi sun hambarar da gwamnatin Francois Bozize. Daga lokacin ne kuma rikicin kasar ya rikide ya koma na addini tsakanin Seleka da anti-balaka Kiristoci.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.