Isa ga babban shafi
Mali

Kasashen duniya sun yi tir da harin Bamako

Kungiyar ta’adda mai alaka da Alqa’ida da ake kira Al Mourabitoun, ta yi ikirarin kai wannan harin da da aka kai a Hotel Radisson da ke birnin Bamako.

Jami'an tsaro a harabar hôtel Radisson, a Bamako, 20 nuwambar 2015.
Jami'an tsaro a harabar hôtel Radisson, a Bamako, 20 nuwambar 2015. REUTERS/Adama Diarra
Talla

Yayin da kasashen duniya suka yi tir da kuma Allah Wadai da hakan, shugaban Amurka Barack Obama, wanda yanzu haka ke halartar taron shugabannin kasashen yankin Asiya da Pasifik, ya yi kakkausar suka a game da wannan hari da aka kai a Bamako.

Shi ma dai bababban magatakarda na MDD Ban Ki-moon, ya ce ya damu matukar a game da halin da kasar ta Mali ta fada a daidai lokacin da kasashen duniya ke kokarin taimaka wa Mali domin komawa kan turbar dimokuradiyya.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.