Isa ga babban shafi
Masar

Masar ta kashe ‘Yan ta’adda 24 a yankin Sinai

Rundunar Sojin kasar Masar tace ta kashe ‘yan ta’adda 24 kusa da inda jirgin saman kasar Russia yayi hadari dauke da fasinjoji 224. Sanarwar sojin tace an kashe mutanen ne a cikin wasu tsaunukan da suka samu mafaka, yayin da aka kama wasu 8 daga cikin su.

Firimiyan Masar Sherif Isma'il ya kai ziyara yankin Sinai da Jirgin Rasha ya tarwatse
Firimiyan Masar Sherif Isma'il ya kai ziyara yankin Sinai da Jirgin Rasha ya tarwatse REUTERS/Stringer
Talla

A yau Talata, Rasha tace ‘Yan ta’adda ne suka tarwatse jirgin fasinjanta a yankin Sinai. Shugaban kasar Vladimir Putin ya sha alwashin gano ‘yan ta’addan tare da murkushe.

Yankin na Sinai na daga cikin inda ake samun tashin hankali a cikin kasar, musamman hare haren ‘Yan ta’ada masu alaka da kungiyar IS da ke da'awar jihadi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.