Isa ga babban shafi
Boko Haram

Deby na Chadi ya ce Boko Haram ta nada sabon Shugaba Muhammad Dawud

Shugaban kasar Chadi Idriss Deby ya ce sun nakkasa Boko Haram kuma suna dab da murkushe ayyukan mayakan kafin karshen shekarar nan. Shugaban kuma ya ce Mayakan sun nada sabon shugaba mai suna Muhammad Dawud.

Shugaban Chadi Idriss Deby
Shugaban Chadi Idriss Deby AFP PHOTO / MIGUEL MEDINA
Talla

A hirarsa da RFI sashen Faransanci, Shugaba Deby ya ce yana da tabbacin za su iya kawo karshen ayyukan kungiyar Boko Haram kafin karshen wannan shekara, domin a yanzu wadansu tisraru kawai ne suka rage a cikin kungiyar.

Shugaban ya ce sun samu labarin Boko Haram ta nada sabon shugaba mai suna Mahammad Dawud a matsayin wanda ya gaji Abubakar Shekau da ake hasashen an kashe shi bayan an dade ba a ji duriyarsa ba.

Deby ya ce sabon shugaban ne ya bukaci a yi tattaunawar sulhu da gwamnatin Najeriya. Amma  Shugaban na Chadi ya ce baya goyon bayan yin sulhu da dan ta’adda.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.