Isa ga babban shafi
Kenya-Amurka

Obama ya yaba da ci gaban da ake samu a nahiyar Afrika

Yau Asabar, shugaban Amurka Barack Obama dake ci gaba da ziyara mai cike da tarihi a kasar Kenya, na ganawa da mahukuntan kasar, kan batutuwan da suka shafi ciniki da zuba jari, gami da yaki da ta’addanci da kuma kare hakkin dan Adam.

Shugaban Amurka Barack Obama, lokacin da ya isa birnin Nairobi
Shugaban Amurka Barack Obama, lokacin da ya isa birnin Nairobi REUTERS/Jonathan Ernst
Talla

Shugaban, dake jawabi a wajen wanin taron bunkasar kasuwanci, ya yaba da yadda nahiyar Africa ke samun ci gaba cikin gaggawa, inda yace ana ana samun bunkasar zuba jari a nahiyar.
Mr. Obama yace mutanen Africa suna samu suna ficewa daga kangin talauci, kudaden shiga na karuwa, ta yadda masu matsakaicin karfi ke samun ci gaba, matasa kuma suna samun ci gaba a bangaren kimiyya don bunkasar harkokin kasuwanci.
Tattaunawar da Obama zai yi da mahukuntan kasar zata mayar da hankali kan barazanar kungiya al-Shebab ta Somalia, mai alaka da Al-Qaeda, da tayi ta kai hare hare a kenya, har da wanda aka hallaka dalidai a wata jami’ar kasar cikin watan Aprilu.
An karfafa matakan tsaro a ciki da wajen birnin Nairobi, inda ofishin jakadancin Amurka a birnin Nairobi ke cewa ‘yan ta’adda zasu iya neman kai farmaki a wajen taron.
Wannan ce ziyararsa ta farko a Kenya, da ita ce tushen mahaifinsa, inda kuma ake sa rai gobe Lahadi zai wuce zuwa kasar Ethiopia.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.