Isa ga babban shafi
Burundi

An kama makamai a kasar Burundi

Jami’an tsaro a kasar Burundi, sun kama mutane 100 bisa zargin su da cewa ‘yan tawaye ne;Yan Sanda sun sanar da karbe makamai da dama ga hanu wasu mutane, a wani mataki na dakile tashe tashen hankula a yayin da ake shirin gudanar da zaben shugabacin kasar. 

Masu adawa da matakin Shugaban kasar Pierre Nkuruziza na Burundi
Masu adawa da matakin Shugaban kasar Pierre Nkuruziza na Burundi Reuters
Talla

Mai Magana da yawu hukumar Tsaron kasar Burundi ya bayana cewa Jami’an tsaron sun karbe kimanin bindigogi 30 a hannun mutanen da ake zargin yan tawayen ne a arewa maso gabashin lardin Muyinga.
Gwamanar lardin na Muyinga, Aline Maniratunga cewa ya yi an kama magoya bayan shugaban ‘yan adawa Agathon Rwasa a samamen da jami’an tsaron suka kai.

Rwasa , shi ne babban dan adawan Shugaban Kasar Pierre Nkrunziza, wanda ke neman zarce wa da mulki a wa’adi na uku.

A dai bangare , jami’an yan Sanda sun bayyana cewa sun kama sama da mutane 80 a areawci kasar Burundi sakamakon rikicin da ya barke a ranar juma’a da ta gabata kusa da iyaka da kasar Rwanda.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.