Isa ga babban shafi
LIBYA

Bangarori masu hamayya da juna a Libya na taro a Maroko

Bangarori masu hamayya da juna a rikicin kasar Libya na gudanar da taro a wannan litinin a kasar Maroko a karkashin inuwar Majalisar Dinkin Duniya a yunkurin da ake na samar da mafita ga rikcin da ake fama da shi tun bayar kawar Muammar Kaddafi daga karagar mulki.

Taron kan Libya a Geneva
Taron kan Libya a Geneva AFP
Talla

Manzon musamman na MDD a kasar ta Libya Bernardino Leon na kokarin samar da yarjejeniya ne a tsakanin bangarorin kafin ranar 17 ga wannan wata da ake shirin fara azumin watan Ramadana.

Yanzu haka dai kasar ta Libya akwai gwamnatoci biyu, majalisun dokokin biyu masu hamayya da juna, yayin da sauran kungiyoyin ‘yan bindiga cikinsu har da magoya bayan Alqaida ke ci gaba da yin iko da wasu yankunan kasar.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.