An sako wasu yan kasar Tunisia a Libya
Ranar Alhamis ne aka sako wasu ‘yan kasar Tunisia 42 da ‘yan bindiga suka yi garkuwa da su a kasar Libya. An dai sako mutanen ne a birnin Tripoli, bayan wata kungiya da ba a bayyana sunan ta ba, suka tsare su tsawon kwanaki.
Wallafawa ranar:
Hukumomin Tunisia sun tsaya kai da fata don gani yan tawayen sun salami yan kasar ta Tunisia da ake tsare da su, ranar litinin da ta gabata, jami’an gwamnatrin kasar ta Tunisia sun bayana cewa mayar Fajr Libya, dake rike da birnin Misrata, suna tsare da ‘yan kasar 172,
Yan tawayen sun sanar da bukatar su na gani hukumomin birnin Tunis su saki wani kwamandan su mai suna Walid el-Klibi, kafin sakin mutanen.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu