Isa ga babban shafi
Najeriya

An kai wa Sarakunan Borno hari

Rahotanni daga Najeriya na cewa Mayakan Boko Haram sun kai wa wasu Sarakunan Gwoza da Uba da Askira hari a Masarautar Borno a lokacin da suke kan hanyarsu zuwa ta'aziyar rasuwar Sarkin Gombe, Wasu rahotannin sun ce 'Yan bindigar sun kashe Sarkin Gwoza Shehu Idris Timta.

Shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau
Shugaban kungiyar Boko Haram, Abubakar Shekau As received by Reuters
Talla

A safiyar Juma’a ne ‘Yan bindigar suka kai wa Sarakunan hari a kan hanyarsu zuwa garin Gombe domin ta’aziyar rasuwar Sarkin Gombe wanda ya rasu a Asibitin London a ranar Talata.

Wata majiya da ke kusa da masarautar Borno ta tabbatar da faruwan al’amarin.

Sanata Ali Ndume Dan Majalisa da ke wakiltar yankin Gwoza a Jahar Borno yace ya tattauna da Sarakunan Askira da Uba amma bai samu ya zanta da Sarkin Gwoza ba da aka ruwaito ‘Yan bindigan sun kashe shi.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.