Isa ga babban shafi
Nijar

An rufe wata jarida a Jamhuriyar Nijar

Hukumomi a birnin Yamai na jamhuriyar Nijar, sun bayar da umurnin rufe wata jarida mai suna Le Courrier, wadda ta shahra wajen sukar lamarin gwmanatin shugaba Issifou Mahamadou.

Shugaban Hukumar sadarwar Jamhuriyar Nijar, Abdourahman Ousman
Shugaban Hukumar sadarwar Jamhuriyar Nijar, Abdourahman Ousman
Talla

Mawallafin jaridar Ali Soumana, ya shaida wa manema labarai cewa ‘yan sanda ne suka rufe ofishin jaridar, to sai dai Ali Soumana ya ce ba wani dalilin da ‘yan sanda suka gabatar dangane da daukar wannan mataki.

Har ila yau ko baya ga jaridar ta Le Courrier, ‘yan sanda sun rufe ofisoshin wasu kungiyoyin kwadago biyu a birnin na Yamai, cikinsu har da kungiyar direbobin motocin Taxi da ta shahra wajen gudanar da yajin aikin neman a rage farashin man fetur a kasar wato kungiyar da ake kira Syncotaxi.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.