Isa ga babban shafi
Faransa-Najeriya

Boko Haram barazana ce ga Yammaci da Tsakiyar Afirka

Shugaba Francois Hollande na kasar Faransa, ya ce dole ne kasashen duniya su hada gwiwa domin kawo karshen ayyukan Boko Haram, kungiyar da ya ce a yau ta zama babbar barazana ga tsaro ga Najeriya da sauran kasashen Yammaci da kuma Tsakiyar Afirka.

Francois Hollande da shugabannin wasu kasashe da ke taro kan Boko Haram
Francois Hollande da shugabannin wasu kasashe da ke taro kan Boko Haram
Talla

Hollande, wanda ke gabatar da jawabi a gaban shugabannin kasashen Najeriya, Nijar, Kamaru, Chadi da kuma Benin da ke halartar taro kan wannan batu a birnin Paris, ya ce ko shakka babu akwai alaka tsakani Boko Haram da kuma kungiyar Aqmi wato reshen Alqa’ida a arewacin Afirka.

Francois Hollande ya ce Faransa ba ta da niyyar tura sojojinta zuwa Najeriya a halin yanzu, amma kuma za ta yi aiki da sauran kasashen duniya domin murkushe ayyukan wannan kungiya.

Taron dai na samun halartar shugaban Najeriya Goodluck Jonathan, da takwaransa Issifou Mahamadou na Jamhuriyar Nijar, da shugaban Chadi Idris Deby Itno, da Bony Yayi na jamhuriyar Benin da kuma Paul Biya na Kamaru.

Har ila yau akwai wakilai daga Birtaniya da kuma Kungiyar tarayyar Turai da ke halartar wannan taro.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.