Niger-Libya
Nijar ta mika Saadi Ghaddafi zuwa Libya
Hukumomi a Jamhuriyar Nijar sun mika dan tsohon shugaban kasar Libya Sa’adi Ghaddafi a hannun hukumomin Tripoli.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Talla
Sa’adi kaddafi, wanda ya gudu daga Libya a shekara ta 2011, ya samu mafaka a birnin Yamai, to amma a yau da safe, kafafen yada labaran Libya sun nuna hotunsa a hannun jami’an tsaron kasar.
Hukumomin kasar ta Libya sun ce za a rike Sa’adi a matsayin fursuna kamar yadda dokar kasa da kasa ta tsara kan fursunoni.
Ana zargin Sa’adi ne da wawure wasu kudaden kasar a lokacin da yake jagorantar hukumar kwallon kafar kasar a Libya.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu