Isa ga babban shafi
Nigeria

An cire dokar hana amfani da wayar sadarwa a jihar Adamawan Najeriya

Hukumomin soja a Tarayyar Najeriya, a jiya alhamis sun amince da bai wa jama’ar jihar Adawa wato daya daga cikin jihohi uku da aka kafawa dokar ta baci, damar yin amfani da wayar sadarwa, bayan share kusan watanni uku a cikin wannan hali.

sojojin Najeriya na shirin zuwa fagen daga
sojojin Najeriya na shirin zuwa fagen daga REUTERS/Tim Cocks
Talla

To sai dai har yanzu sauran jihohi biyu da wannan doka ta shafa wato Yobe da Borno, kamar yadda kakakin rundunar tsaron Najeriya Burgediya Janar Chris Olukolade ya shaida wa sashen Hausa na RFI, za su ci gaba da kasancewa a karkashin dokar da ke haramta yin amfani da hanyioyin na sadarwa.
Daukar matakin sassauta dokar a jihar Adamawa ya biyo bayan ci gaban da aka sama ne da kyautatuwar tsaro a jihar a cewar Janar Olukolade.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.