Isa ga babban shafi
Faransa-Afrika

Faransa za ta karfafa dangantaka da kasashen Afrika a taron Congo

Shugaban kasar Faransa Francois Hollande zai nemi karfafa dangantakar kasuwanci da Diflomasiya da kasashen Afrika masu Magana da harshen Faransanci a wani taro da kasashen tare da Faransa za su gudanar a Jamhuriyyar Demokradiyyar Congo.

Shugaban kasar Faransa, François Hollande
Shugaban kasar Faransa, François Hollande REUTERS/Darrin Zammit Lupi
Talla

Kimanin Kasashen Afrika masu Magana da harshen Faransanci 70 ne ake sa ran za su kai ziyara birnin Kinshasha domin halartar taron na kwanaki biyu inda kasashen za su yi kokarin fito da hanyoyin magance rikicin ‘Yan tawayen Congo da Mali.

Shugaban Faransa Francois Hollande ya yi alkawalin taimakawa ga ci gaban Demokradiyya a Afrika da ke fama da magudin zabe.

Kasar Faransa dai tana cikin manyan kasashe da ke zuba hannayen jari a kasashen Afrika. kuma duk da matsalar tattalin arziki da ya shafi kasar amma Faransa tana taka rawa wajen taimakawa da dakarun Soji musamman a kasashen Senegal da Chad da Cote d'Ivoire da Djibouti.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.