Isa ga babban shafi
Amurka-Najeriya

Amurka ta yi gargadin Boko Haram suna shirin kai hare hare a Abuja

Ofishin Jekadancin Amurka a Najeriya ya yi gargadin kungiyar Boko Haram Suna shirin kai hare hare a birnin Abuja a wuraren shakatawar Turawa a wani sako da Ofishin ya yada a Intanet.

Imam Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Boko Haram.
Imam Abubakar Shekau, Shugaban Kungiyar Boko Haram. Reuters
Talla

“Ofishin jekadancin Amurka ya samu sakon kungiyar Boko Haram sun shirin kai hare hare a Abuja, Najeriya a wuraren da Turawa ke sauka,” Sakon gargadi da Amurka ta yi ga Amurkawa.

A watan Nuwamba Amurka ta aiko da irin wannan gargadin wanda ya janyo suka amma babu wani hari da aka samu a birnin Abuja a lokacin.

A Najeriya an dade ana zargin Kungiyar Boko Haram da kai hare hare a arewacin kasar inda kungiyar kare Hakkin Bil'adama ta Amnesty International  tace kungiyar Boko Haram ta kashe mutane sama da 1,000 tun fara kaddamar da hare hare a shekarar 2009.
 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.