Isa ga babban shafi
Najariya

Jonathan ya gana da Manyan Jami’an tsaro

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan ya yi wata ganawar gaggawa da Jami’an tsaron kasar domin tattauna matsalar tsaro a kasar musamman game da hare haren da aka kai a ranar Kirsemeti. Shugaban yana kokarin lalubo hanyar magance zubar da jinin ‘Yan Najeriya, inda ake saran kara kaimi don magance matsalar tsaro da ke barazana ga al’ummar kasar. 

Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan
Shugaban Najeriya Goodluck Jonathan RFI
Talla

03:13

Abubakar Tsav, Tsohon kwamishinan 'Yan Sandan Lagos

Garba Aliyu

A lokacin da yake ganawa da Manema Labarai, Sufeto Janar na ‘Yan Sanda Hafiz Ringim, yace shugaba Jonathan ya damu matuka game da kalubalen tsaro da ke addabar Najeriya, akan haka ne ya gayyace su domin tattauna yadda zasu shawo kan matsalar.

Ana kalubalantar gwamnatin Jonathan wajen rashin shawo kan matsalar Kungiyar Boko Harama. Da ake zargin kaddamar da hare hare a Arewacin Najeriya da birnin Abuja babban birnin kasar.

05:39

Barr. Solomon Dalung

Bashir Ibrahim Idris

A ranar Talata wasu wadanda ba’a tantance ba sun kai wani hari a makarantar Islama a kudancin kasar Jahar Delta, wanda y yi sanadiyar raunata yara kanana guda bakwai.

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.