Isa ga babban shafi
Koriya ta Arewa

Koriya ta Arewa ta sake gwajin makami mai linzami

Koriya ta Kudu ta ce, Koriya ta Arewa ta sake gwajin wasu makamai biyu masu linzami da suka yi tafiyar kilomita kusan 250 a sararin samaniya kafin fadawa cikin teku.

Sau biyu kenan da Koriya ta Arewa ke gwajin makamai masu linzami cikin kasa da mako guda
Sau biyu kenan da Koriya ta Arewa ke gwajin makamai masu linzami cikin kasa da mako guda AFP PHOTO/KCNA VIA KNS
Talla

Babban Hafsan Sojin Koriya ta Kudu ya ce, an harba makaman ne daga yankin Wonsan da ke Gabashin gabar ruwan kasar, inda ya ce, wadannan gwaje- gwaje ba za su taimaka wajen samun zaman lafiya a yankin ba.

Koriya ta Arewa ta ce, gwajin wani gargadi ne kan shirin atisayen soji da Koriya ta Kudu da Amurka ke shirin yi a Yankin.

A karkashin wani kuduri, Kwamitin Sulhu na Majalisar Dinkin Duniya ya haramta wa Koriya ta Arewa gwajin makamai masu linzami, amma sau biyu kenan da kasar ta yi gwaje-gwajen makaman a cikin kasa da mako guda duk kuwa da ganawar da aka yi tsakanin shugaban kasar da takwaransa na Amurka, Donald Trump a watan jiya.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.