Majalisar Dinkin Duniya
Rahoto kan bikin ranar Yan Jaridu ta duniya
UKU ga watan Mayu na kowace shekara rana ce da Majalisar Dinkin Duniya ta ware don gudanar da bikin 'yancin da kare hakkin manema labarai inda ake nazari kan hanyoyin da za a tabbatar da 'yancin Yan Jaridun, tare da sake mara musu baya don gudanar da ayyukansu kamar yadda yarjeniyoyi na kasa da kasa suka tabbatar.Taken Bikin bana dai shi ne “Kafofin yada labarai da Demokradiyya, aikin manema labarai da zabuka a lokacin da ake jirkita labarai”.Daga Maiduguri, wakilinmu Bilyaminu Yusuf ya hada mana rahoto akan wannan rana.
Wallafawa ranar: