Mutane Da Yawa Sun Kasa Numfashi A Yankin Da Ake Yaki A Syria
A Kasar Syria mutane masu tarin yawa ne aka basu kulawa ta musamman da magunguna cikin gaggawa yankin Ghouta saboda matsalolin rashin iya numfashi a wuraren da ake tafka yaki wanda ya sa jami'an lafiya fargaban an yi amfani da makamai masu guba ne.
Wallafawa ranar:
Kungiyoyin dake sa idanu akan wannan yaki na cewa mutane akalla 60 suka shiga wannan matsala a yankin garuruwan Saqba da Hammuriyeh bayan wani harin Bam da aka kai
Likitoci a wani wajen kulka da mutane da suka jikkata a Gabashin Ghouta sun ce sun baiwa mutane 29 magunguna na alamun sun shaki guba da aka watsa a inda suke.
Kungiyoyin basu bayyana an sami rasa rai ba ya zuwa yanzu.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu