Isa ga babban shafi
DRC

'Yan bindiga sun kashe dakarun wanzar da zaman lafiya a Congo

Akalla dakarun wanzar da zaman lafiya na majalisar dinkin duniya guda 14 da sojojin Congo guda 5 ne wasu da ake zargin 'yan bindiga ne suka hallaka sakamakon wani hari da suka kai a wani sansani da ke gabashin kasar Congo.

Dakarun wanzar da tsaro na majalisar dinkin duniya a DRC.
Dakarun wanzar da tsaro na majalisar dinkin duniya a DRC. cfr.org
Talla

Sakatare-janar na majalisar dinkin duniya Antonio Giuterres ya ce rahotanni da aka fara samu sun nuna cewa dakaru guda 14 da suka fito daga kasar Tanzania ne aka kashe a yammacin ranar Alhamis a arewacin Kivu da ke gabashin Congo.

Wasu dakarun guda 53 ne aka raunata, yayin da 4 daga cikinsu ke cikin mawuyacin hali.

A cikin sanarwar da ya fitar, Antonio Guterres ya bayyana al’amarin a matsayin laifin yaki wanda ba za a amince da shi ba.

Ya kuma yi kira ga kasar ta jamhuriyar demokradiyyar Congo da ta yi bincike sannan ta hukunta wadanda suka aikata kisan.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.