Isa ga babban shafi
Najeriya

Sojan Najeriya Sun Kama Wani Jagoran Boko Haram

Rundunar sojan Najeriya ta sanar da cewa ta kama wani kasaitaccen dan kungiyar Boko Haram da ake ta nema na tsawon wani lokaci.

Babban Hafsan Sojan Najeriya Tukur Buratai
Babban Hafsan Sojan Najeriya Tukur Buratai AFP PHOTO/STRINGER
Talla

Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Brigadier Sani Usman Kukasheka ya fadi cikin wata sanarwa cewa mutumin mai suna Aliyu Ahmed wanda aka fi sani da Aliko an kamashi da makamai a kauyen Yuga dake Karamar Hukumar Toro a Jihar Bauchi inda yake buya.

A cewar Sojan Najeriya an same shi da bindiga babba da karama kuma ya amsa cewa akwai shi da bindiga  kirar AK-47 amma ta bace a lokacin da suka gwabza fada a bara.

Sojan Najeriya sun kuma sanar da kama wasu mutane hudu masu safarar yara kana a jihar Yobe domin an same su da yara  kanana 19.

 

 

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.