Sojan Najeriya Sun Kama Wani Jagoran Boko Haram
Rundunar sojan Najeriya ta sanar da cewa ta kama wani kasaitaccen dan kungiyar Boko Haram da ake ta nema na tsawon wani lokaci.
Wallafawa ranar:
Daraktan Hulda da Jama’a na Rundunar Brigadier Sani Usman Kukasheka ya fadi cikin wata sanarwa cewa mutumin mai suna Aliyu Ahmed wanda aka fi sani da Aliko an kamashi da makamai a kauyen Yuga dake Karamar Hukumar Toro a Jihar Bauchi inda yake buya.
A cewar Sojan Najeriya an same shi da bindiga babba da karama kuma ya amsa cewa akwai shi da bindiga kirar AK-47 amma ta bace a lokacin da suka gwabza fada a bara.
Sojan Najeriya sun kuma sanar da kama wasu mutane hudu masu safarar yara kana a jihar Yobe domin an same su da yara kanana 19.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu