Isa ga babban shafi

Liverpool ta karbi jagorancin teburin Firimiya bayan doke Burnley

Kungiyar kwallon kafa ta Liverpool ta koma jagorancin  teburin Firimiyar Ingila bayan doke Burnley da kwallaye 2 da nema a haduwarsu ta daren jiya Talata.

Dan wasan Liverpool Mohamed Salah.
Dan wasan Liverpool Mohamed Salah. POOL/AFP
Talla

Kwallayen wanda Reds ta samu ta hannun ‘yan wasa Darwin Nunez a minti na 6 da fara wasa da kuma Diago Jota a minti na 90 gab da tashi daga wasa sun baiwa tawagar ta Jurgen Klopp damar kara yawan makinta zuwa 42 banbancin maki 2 tsakaninta da Arsenal wadda ke da wasa guda a hannu.

Wasan wanda ya gudana a gidan Burnley Liverpool ta samu nasarar ne duk da soke kwallon Harvey Elliot wadda ya ci da taimakon Mohamed Salah bayan da rafali ya bayyana ta a matsayin ta satar fage.

Liverpool na fuskantar kalubale daga Arsenal wadda kje Shirin haduwa da West Ham a gobe Alhamis, wanda matukar ta yi nasara a karawar kenan dole Reds ta koma matsayin ta 2.

Kafin haduwar ta jiya dai Burnley na matsayin ta 17 ne a teburin na Firimiya yayinda bayan rashin nasarar ta jiya kai tsaye ta koma ta 19.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.