Isa ga babban shafi
Wasanni-Kwallon kafa

Kungiyoyi 32 za su fara fafatawa a gasar cin kofin zakarun Turai

Yau Talata ne za a fara wasannin gasar cin kofin zakarun Turai, gasar da za a fafata tsakanin kungiyoyin kwallon kafar nahiyar ta Turai guda 32, wadanda aka kasa zuwa rukuni 8 dauke da kungiyoyi hur-hudu.

Tambarin gasar cin kofin zakarun Turai
Tambarin gasar cin kofin zakarun Turai REUTERS/Eric Gaillard
Talla

Tun a jiya Litinin ne dai aka ga Lionel Messi na Barcelona ya koma filin atisaye bayan fama da jinya gabanin wasan na su na yau da za su kara da Borussia Dortmund a rukuin F.

Tun bayan wasanninsa na Copa America da Messin ya dokawa kasarsa Argentina cikin watan Yuli ba a sake ganin keyar Kaftin din na Barcelona a fili ba, inda ya rasa wasanni 4 na farkon wannan kaka, matakin da ya sanya Barcelonar rashin nasara a 2 daga cikin wasanninta 4 lokacin da baya nan.

To baya ga wasannin na Barcelona da Borussia Dortmund da kuma Inter Milan da Slavia Prague a rukunin F, akwai wasan Napoli da Liverpool baya ga Salzburg da KRC Genk a rukunin E.

A rukunin G akwai wasan Lyon da Zenit St Petersburg, kana wasan Benfica da RB Leipzig.

A rukunin H kuwa akwai wasan Ajax da Lille kana Chelsea da Valencia.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.