Isa ga babban shafi

Ba ma fargabar jadawalin gasar zakarun Turai- Klopp

Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Liverpool Jurgen Klopp ya ce bai sa a ransa dole sai Club din ya sake dage kofin zakarun Turai a bana ba, bayan nasararsa ta dage kofin a bara da nasarar kwallaye 2 da banza kan Tottenham.

Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Liverpool Jurgen Klopp
Mai horar da kungiyar kwallon kafa ta Liverpool Jurgen Klopp Reuters
Talla

A cewar Klopp wanda ke jawabin gabanin fitar da jadawalin gasar a yau, ya ce akwai kungiyoyi da dama da suka cancanci dage kofin ba Liverpool kadai ba.

Jurgen Klopp ya ce baya fargabar kai wa wasan karshe na bana karkashin gasar cin kofin na zakarun Turai da zai gudana ranar 30 ga watan Mayun 2021 filin wasa na birnin Santanbul da ke turkiya, sai dai ya ce Liverpool na da cikakkiyar dama ne kwatankwacin wadda kowanne Club cikin kungiyoyin kwallon kafa 26 da za su fafata a gasar ke da shi.

Kalaman na Klopp dai na zuwa ne a dai dai lokacin da Liverpool din ke jerin tawagar farko da ake kyautata zaton iya lashe kofin na bana.

Rukunin farko dai da hasashen ya nuna cewa za su iya dage kofin sun kunshi ita Liverpool din kana Barcelona wadda Livertool ta fitar a wasan gab dana karshe a bara, sai kuma Manchester City babbar abokiyar dabin Liverpool kuma mai rike da kofin Firimiya kana PSG Juventus Real Madrid dsa kuma Tottenham wadda tasha kaye hannun Liverpool a wasan karshe na dage kofin.

LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.

Ku saurari dukannin labaran duniya ta hanyar sauke man hajar RFI

Rarbawa :
Babu shafi

Babu bayanan da ka bukata ko kuma sam babu su.