Najeriya za ta fafata da Kamaru a wasan kusa dana karshe
Yau Talata tawagar ‘yan wasan Najeriya Super Falcons za su fafata wasan kusa dana karshe da Kamaru a gasar cin kofin nahiyar Afrika ajin mata.
Wallafawa ranar: Chanzawa ranar:
Duk wanda ya samu nasarar kaiwa matakin wasan karshe, tsakanin Najeriya da Kamaru, to shi ne zai halarci gasar kwallon kafar cin kofin duniya ajin mata, da Faransa za ta karbi bakunci a shekarar 2019.
Da fari dai Najeriya mai rike da kofunan gasar nahiyar afirka ajin mata har guda takwas, ta soma gasar bana ce da kara hagu, inda Afrika ta kudu ta samu nasara kanta da kwallo 1-0.
Amma daga bisani a sauran wasanninta na rukuni, Najeriya ta lallasa Zambia da kwallye 4-0, sai kuma Equatorial Guinea da Najeriyar ta lallasa da kwallaye 6-0.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu