Jamus ta lashe kofin zakarun Nahiyoyi
Jamus ta lashe kofin gasar zakarun nahiyoyi bayan ta samu sa’ar Chile ci 1-0 a karawar karshe da suka yi a jiya a Saint Petersburg na Rasha. Portugal ce ta zo matsayi na uku bayan ta doke Mexico.
Wallafawa ranar:
Mai tsaron baya na Chile Marcelo Diaz ne ya yi babban kuskuren da ya ba Stindi na Jamus nasarar jefa kwallo a ragar Bravo na Manchester United.
Chile dai ta kai wa Jamus hare hare, kuma ta fi yawan taba kwallo da kusan kashi 61, tare da kai hari 20 a gidan Jamus.
Julian Drexler ne aka ba kyautar gwarzon dan wasa a gasar da aka fafata tsakanin kasashe 8 zakaru a nahiyoyin duniya hadi da Rasha da ta karbi bakuncin gasar.
Wannan ne karo na fartko da Jamus ta lashe kofin gasar.
Portugal ce ta zo na uku a gasar bayan ta doke Mexico ci 2-1.
LabaranSamun Labaran RFI, Hirarraki, Rubattattuun Labarai, Labarai game da wani, shirye-shirye.
Hulda da mu